Labarai
IPAC ta yaba da hana yada hirar siyasa kai tsaye a Kano

Hadakar kungiyoyin jam’iyyun Siyasa na Najeriya IPAC ta ce, za ta hadakai da jami’an tsaro da dukkan masu ruwa da tsaki a fannin siyasa wajen ganin an hukunta duk wanda ya shiga wata kafar yada labarai ya ci zarafin wani ba tare da hakkinsa ba.
Shugaban hadakar kungiyoyin na Kano Alhaji Isah Nuhu Isah, ne ya bayyana hakan a zantawarsa da Freedom Radio.
Haka kuma, ya yaba wa matakin da shugabannin gidajen Radio da Talabijin na Kano suka dauka na daina yada duk wata hirar siyasa kai tsaye ba tare da an tantance ta ba.
You must be logged in to post a comment Login