Connect with us

Labarai

Jagoran adawar Kamaru Issa Bakary ya yi iƙirarin lashe zaɓen shugaban ƙasa

Published

on

Jagoran adawar kasar Kamaru Issa Tchiroma Bakary, ya yi iƙirari samun nasara a zaɓen shugaban ƙasar da aka gudanar ranar Lahadi.

Cikin wani bidiyo da ya fitar, da tsakar daren da ya gabata, Bakary ya gode wa al’ummar Kamaru kan yadda suka samar da canji da ya ce sun yi a ƙasar, iƙirarin nasa na zuwa ne a daidai lokacin da hukumar zaɓen ƙasar ke ci gaba da tattara sakamakon zaɓukan.

Bakary ya ce, cikin girmamawa da nutsuwa al’ummar Kamaru sun yi zaɓinsu, don haka ya kamata a martaba zaɓinsu, da ya alƙawarta wallafa cikakken sakamakon zaɓukan daga rumfunan zaɓen ƙasar.

Kawo yanzu hukumomin Kamaru ba su ce komai ba game da iƙirarin jagorar adawar, to amma a baya ministan cikin gida na ƙasar, Paul Atanga Nji ya nanata haramcin iƙirarin nasara daga ɗaiɗaikun ƴantakara tare da wallafa abin da ya kira haramtaccensakamakon zaɓe.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!