Connect with us

Labarai

Jami’an tsaro sun kama mota dauke da karafunan titin jirgin kasa

Published

on

Hukumar tsaron Civil Defence a Jihar Bauchi ta kama wata babbar mota da ke ɗauke da layukan dogon jirgin kasa da ake zargin an sato, tare da kama mutane biyar da ake zargi da aikata laifin.

Ta cikin wata sanarwa da mai magana da yawun hukumar, Saminu Yusuf, ya fitar ta ce, an cafke motar ne bayan samun bayanan sirri, a hanyar Miri zuwa Jos, kusa da Gital a ƙaramar hukumar Tafawa Balewa, yayin da ake ci gaba da neman direban motar da sauran masu dakon kayan da suka tsere.

Kwamandan na Civil Defence a jihar, Oloyede Nelson, ya jaddada ƙudirin hukumar na kare muhimman kadarorin ƙasa tare da yaƙi da ɓarna, yana mai kira ga al’umma su rika bai wa hukumomin tsaro sahihan bayanai duk lokacin da suka ga motsi da basu aminta da shi ba.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!