Connect with us

Labarai

Jami’an tsaro na hadin gwiwa 5000 ke yaki da ta’addanci a Arewa maso gabashin Najeriya – Sufeto

Published

on

Sufeto Janar na ‘yan sandan kasar nan Usman Baba Alkali, ya ce, jami’an ‘yan sanda da sojoji akalla dubu biyar ne ke aikin yaki da ta’addanci a yankin Arewa maso gabashin kasar nan.

Usman Baba Alkali ya yi wannan jawabi ne jiya Litinin 5 ga watan Yuli a shelkwatar ‘yan sanda da ke birnin tarayya Abuja, lokacin da ya karbi bakuncin kungiyar matan jami’an tsaro ta kasa karkashin jagorancin shugabarta Mrs Victoria Irabor.

Babban sufeton ‘yan sandan, ya ce, ‘yan sanda da sojoji suna aikin hadin gwiwa don magance matsalolin tsaro a arewacin kasar nan da ma Najeriya baki-daya, har ma da aikin wanzar da zaman lafiya a kasashen waje.

A na ta jawabin Mrs Vctoria Irabor, ta ce sun ziyarci babban sufeton ‘yan sandan ne domin karfafawa jami’an tsaron kasar gwiwa wajen gudanar da aikinsu yadda ya kamata.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!