Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

ilimi

Jami’ar Dutsen jihar Jigawa za ta fara koyar da harkokin shari’a da injiniya

Published

on

Jami’ar tarayya da ke Dutsen jihar Jigawa ta shirya tsaf don koyar da fannin harkokin shari’a da Injiniya kari kan wadanda ta ke da su.

Jami’ar ta ce tana aiki don samar da cibiya guda daya wacce za ta kula da bincike kan dukkan bangarorin karatun dalibai a jami’ar tare da bangarori daban-daban kamar su sashin tarbiyya da bangaren bada shawara kan harkokin kudi.

Sai kuma bangaren da zai rika saurarar koken dalibai da kuma samun gurbin karatu da sauran korafe-korafe.s

Shugaban jami’ar, Farfesa Abdulkarim Sabo Mohammed ne ya bayyana hakan a jiya Laraba a wani taron tattaunawa da ‘yan jarida don bayyana wasu muhimman ayyukan da za su kara bunkasa makarantar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!