Connect with us

Labarai

Jam’iyyar ADC ta sanya 14 ga Afrilu domin babban taron ta na kasa

Published

on

Jam’iyyar adawa ta ADC ta sanar da cewa za ta gudanar da babban taronta na kasa a ranar 14 ga Afrilu, 2026, domin zaben sabbin shugabannin jam’iyyar na kasa.

A cikin wata sanarwa da kakakin jam’iyyar, Bolaji Abdullahi, ya fitar, ya ce an tsara jerin tarukan zaben shugabanni daga matakan kasa da kasa na jam’iyyar domin sabunta shugabanci kamar yadda kundin tsarin jam’iyyar ya tanada.

Sanarwar ta ce za a fara da tarukan zaben shugabanni a rumfunan zabe da unguwanni ranar 7 ga Afrilu, sai na kananan hukumomi a ranar 9 ga Afrilu, sannan na jihohi a ranar 11 ga Afrilu, kafin a kammala da babban taron kasa a ranar 14 ga Afrilu.

Jam’iyyar ta ce wannan tsari na daga cikin kokarinta na karfafa dimokuradiyya a cikin jam’iyyar, tare da shirye-shiryen tunkarar zaben shekarar 2027.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!