Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Jam’iyyar APC ta naɗa Jamila Mai Wuƙa muƙamin SA

Published

on

Ofishin shugabar Matan Jam’iyyar APC ta ƙasa Mrs Mary ta nada Jamila Ado Mai Wuƙa a matsayin mashawarciya kan harkokin yaɗa labarai a yankin Arewa.

Hakan na ƙunshe ne ta cikin wata sanarwa da Sakataren Ofishin shugabar Matan APC ta ƙasa Olugbenga Pius, ya fitar.

Sanarwar ta ruwaito cewa, naɗin ya zo a matsayin shaida ƙarara na ƙwazon aiki da jajircewar Jamila.

A cewar sanarwar, ƙwazon nata zai yi amfani matuƙa ga ofishin shugabar mata a jam’iyyar APC ta ƙasa.

Ofishin ya taya Jamila Ado maiwuka murnar samun wannan sabon ofishi a matsayin mashawarciya kan harkokin yada labarai SA a ofishin shugabar mata ta jam’iyyar APC ta kasa Mrs Mary Alile.

Sanarwar ta bukaci SA ta ci gaba da jajircewa wajen ganin an samar da ci gaba a jam’iyyar APC.

A cikin sanarwar ta yi Addu’a kan Allah ya ba su ƙarfi da basira don gudanar da ayyukan su a wannan ofishi.

Har zuwa naɗin nata, Jamila Ado Mai Wuƙa ta kasance ma’aikaciya a tashar Freedom Radio Kano.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!