Connect with us

Labarai

Jigawa: Yan sanda sun cafke mutane 13 da ake zargi da aikata manyan laifuka

Published

on

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Jigawa ta tabbatar da kama mutane 13 ciki har da  mutane biyar da hukumar ta ke nema ruwa a jallo, bisa zargin su damfrar jama’a ta hanyar canjin kudaden ketare.

 

Rundunar, ta bayyana hakan ne ta cikin wata sanarwa da mataimakin jami’in hulda da jama’a na rundunar ASP Ibrahim Idris, ya fitar a ranar Laraba.

Sanarwar ta ce, bayan korafe-korafe kan wadanda ake zargi kan laifin damfara fashi da makami da kuma sauran munanan laifuka, ya sanya rundunar yan sandan ta hada hannu da jami’an soji, da kuma yan sandan farin kaya na DSS, gami da jami’an Civil defence

 

Daga cikin wadanda aka kama sun hada da Salisu Ibrahim, da Umar Dauda, Abdullahi Umar, sai kuam Magaji A. Mohd da kuma  Abubakar Ibrahim.

 

Yayin sumamen dai, hukumomin sun samu nasarar kama takardun kudade da suka hada da Naira, da kuma dalar Amurka baya ga wayoyin hannu sama da guda biyar, sai katin sahaidar zama dan kasa.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!