Connect with us

Labarai

Jigawa: Yan sanda sun kama matasa 3 bisa zargin su da safarar kwayoyi

Published

on

Rundunar ‘yan sandan jihar Jigawa, ta kama wasu matasa uku da ta ke zargi da safarar miyagun kwayoyi a fadin jihar.

Hakan na cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar ya fitar SP Shisu Lawan Adam, ya fitar yau Talata a birnin  Dutse.

SP Shisu Lawan,  ya kuma ce an kama wadanda ake zargin ne a ranar 18 ga watan Oktoban nan da muke ciki a Garki da Fagam da Maigatari, inda suka kama miyagun kwayoyin da adadin su ya kai 23,944 wadanda ake zargin dai daya ya fito daga Jihar Kano yayin da dayan kuma ya fito daga jamhuriyar Nijar.

Rundunar ta kuma bayyana cewa, yanzu haka matasan da ake zargin su na sashen binciken laifukan miyagun kwayoyi domin ci gaba da  bincike.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!