Connect with us

Labarai

Jirgin Kasan da ya tashi daga Kaduna zuwa Abuja ya yi hatsari

Published

on

Rahotonni daga jihar Kaduna na cewa wani jirgin kasa da ke kan hanyar zuwa Abuja ya yi hadari a safiyar Litinin.

 

Sai dai, rahotonni sun bayyana cewa, ba a samu asarar rayuka ba, sai dai jikkatar da mutane da dama su ka yi.

 

A cewar wasu da hadarin jirgin kasan ya ritsa da su, an sanya karin Ttarago ne lokacin da jirgin ya isa Jere, lamarin da ya haddasa hatsarin.

 

Bayanai sun ce, an dauki tsawon lokaci gabanin gyara jirgin tare da ci gaba da tafiya zuwa birnin tarayya Abuja.

 

A cewar shaidun gani da ido, dimbin fasinjan jirgin sun galabaita yayin da suke a firgice saboda fargabar abin da ka je ya zo.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!