Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Jiri ne ya ɗebe ne a lokacin da na ke jawabi a fadar shugaban ƙasa – Abdurrashid Bawa

Published

on

Shugaban hukumar yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa zagon ƙasa EFCC Abdurrashid Bawa ya ce, likitoci sun tabbatar da cewa ya samu ƙarancin ruwa a jikin sa, a daidai lokacin da yake jawabi a fadar shugaban ƙasa.

Abdurrashid Bawa ya bayyana hakan lokacin da ake hira da shi a gidan talabijin na Channels awanni kaɗan bayan farfaɗowar sa.

Bawa ya ce ‘lokacin da lamarin zai faru Na fara jin jiri, sai kuma Na yanke jiki Na faɗi, lamarin da ya janyo hanakalin jama’ar gurin suka ba ni ɗaukin gaggawa”.

Idan za a iya tunawa da safiyar ranar Alhamis ne shugaban EFCC ɗin ya yanke jiki ya faɗi a fadar shugaban ƙasa, daidai lokacin da yake bayani a wani ɓangare na bikin ranar katin ɗan ƙasa.

Abdurrashed Bawa ya kuma ce, ya samu lafiya tun bayan da ya samu kulawa daga wajen likitoci, har ma ya koma bakin aiki.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!