Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Kotu ta umarci ƙungiyar likitoci masu neman ƙwarewa su janye yajin aiki da su ke yi cikin gaggawa

Published

on

Kotun ɗa’ar ma’aikata ta ƙasa da ke zaman ta a Abuja ta umarci ƙungiyar Likitoci masu neman kwarewa NARD, da ta janye yajin aikin da ta fara tun ranar 2 ga watan Agusta.

A zaman kotun na yau Juma’a mai shari’a Bashir Alkali ya umarci ƙungiyar NARD ta dakatar da yajin aikin da ta ke yi cikin gaggawa, bayan da ya saurari dukkanin ɓangarorin da lamarin ya shafa.

Umurnin ya biyo bayan ƙarar da gwamnatin tarayya ta shigar gaban kotun domin ƙalubalantar halaccin yajin aikin na su.

Tuni dai gwamnatin tarayya da ma’aikatar lafiya ta ƙasa suka dage kan cewa, kungiyar NARD ta fara yajin aikin a daidai lokacin da bai dace ba, kuma ba su yi shi akan ƙa’ida ba.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!