Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Wasanni

Jonathan ya bude sabon filin wasanni a Yenagoa

Published

on

Tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan ya kaddamar da sabon wajen gudanar da wasanni mai suna GEJ Sports Club don samar da matasan ‘yan wasa masu hazaka a Najeriya.

Jonathan ya kuma nemi hadin gwiwar masu ruwa da tsaki a harkokin wasanni yayin taron kaddamarwar a garin Yenagoa dake jihar Bayelsa.

Ya ce, samun hadin gwiwa daga masu ruwa da tsaki da abin ya shafa zai taimaka wajen kula da kuma bunkasa hazikan matasa da za a yi gogayya da su a fagen wasanni a fadin duniya.

Ya kuma yaba wa wadanda suka halarci taron, kamar yadda ya bayyana cewa GEJ Club House za ci gaba da karɓar bakuncin wasannin cikin gida daban-daban.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!