Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Kafa Masaku zai bunkasa tattalin arzikin kasa -MD

Published

on

Kamfanin Mudassir and brothers da ke nan Kano, ya ce zai samar da wata masaka a wani yunkuri na samarwa matasan jihar Kano aikin yi.

Shugaban kamfanin Alhaji Mudassir Idris Abubakar ne ya bayyana hakan yau, jim kadan bayan kammala shirin Barka da Hantsi na nan tashar Freedom Radiyo, wanda ya yi duba kan inganta masana’atun cikin gida da suka jima da durkushewa.

Alhaji mudassir Idris ya kuma ce, rufe iyakokin kasar nan ya kawo cigaba  matuka ta fuskar bukansa tattalin arzikin kasa.

Batutuwa masu nasaba

kamfanoni 30 ne suka aike da bukatar karbar jinginar ma’aikatar albarkatun ruwa

Hukumar kula da kamfanoni sadarwa ta ce ta gano yadda ake cirewa kwastamomi kudade babu gaira babu dalili

Tsohon gwamnan bankin CBN ya ce kamata yayi a samar da asusun tallafawa kananan masana’antu

A na sa bangaren, shugaban masakar Adhama textile, Alhaji Sa’idu Dattijo Adhama, ya ce, kafa kamfanonin masaku a jihar nan na da alfanu sosai musamman na Auduga wanda ya ke da matukar amfani.

Bakin dai sun yi kira ga gwamnati tarayya da na jihohi da su tallafa musu wajen kawo ci gaban masana’antu a fadin kasar nan, don fadada komar tattalin azikin kasar da kuma samar da aikin yi ga al’umma.

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!