Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Kamfanin NNPC sun fara safarar man fetur kasashen Burkina Faso da Mali da Cote d’Ivore

Published

on

Kamfanin mai na kasa (NNPC), ya ce, masu fasakwaurin man fetur a kasar nan suna safarar sa zuwa kasashen Burkina faso da Mali da kuma Cote d’Ivoire.

 

A cewar kamfanin na (NNPC), ‘yan fasakwaurin suna kuma safarar man fetur din zuwa kasar Ghana domin sayar da shi su ci riba.

 

Babban jami’in gudanarwar kamfanin na NNPC Henry Ikem-Obih ne ya bayyana haka ga manema labarai jiya a Abuja.

 

Ya ce, yayin da ake sayar da farashin Litar man fetur akan naira dari da arba’in da biyar a kasar  nan a sauran kasashen da ke makwabtaka da kasar nan, ana sayarwa akan naira dari uku da hamsin da kuma dari hudu da talatin.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!