Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Kananan yara miliyan 12 ne ke fama da yunwa a Najeriya – Minista

Published

on

Gwamnatin tarayya ta ce kimanin kananan yara milyan 12 ne ke cikin matsalar rashin wadataccen abinci.

Ma’aikatar aikin gona da raya karkara ce ta tarayya ta bayyana hakan ta bakin ministan aikin gona Alhaji Sabo Muhammad Nanono yayin zantawa da manema labarai wanda mai bashi shawara Dr. Adeyinka Onabolu ya wakilce shi, a birnin Abeokuta na jihar Ogun.

Ta cikin jawabin nasa Alhaji Sabo Nanono ya kara da cewa, tuni gwamnatin tarayya ke ci gaba da yin kokarin samar da wadataccen abinci ga kananan yara a fadin kasa baki daya.

Ya kara da cewa, kaso 37% na kananan na fama da matsalar yunwa wadda ke haifar musu da matsala ta rashin girma a sakamakon rashin wadataccen abinci mai gina jiki.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!