Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Kano: Ƴan sanda sun cafke mai buga jabun takardun ɗaukar aiki

Published

on

Rundunar ‘yan sanda jihar Kano ta kama wani mutum da ya kware wajen buga takardun daukar aiki na bogi.

Mutumin mai suna Rabi’u Sani mazaunin karamar hukumar Dala mai shekara 62 ya amsa laifin da ake zarginsa da shi a gaban rundunar Yan sandan.

Ya ce shi da abokan su 3 sun dade suna wannan sana’a ta buga takardun daukar aiki na bogi suna sayarwa ga masu neman aiki.

Da yake bayanin yadda wannan gurbatacciyar sana’ar tasu take, Rabi’u Sani ya ce masu neman aiki a ma’aikatar ilimi suke siyarwa da takardar, tare da karbar kudi da ya kama daga dubu 40 zuwa 60.

Mai magana da yawun rundunar Yan sandan jihar Kano DSP Abdullah Haruna Kiyawa ya ce sun sami korafi daga wata mata wadda ya karbi kudinta ya bata takardar ta bogi tsahon watanni biyar ba tare da ta ga albashi ba.

Abdullahi Kiyawa ya ce sun sami mai laifin da takardar bogin guda 30 tare da kudi kimanin miliyan 3 da dubu dari takwas a hannunsa baya ga wasu kudaden kimanin miliyan daya da dubu dari biyu.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!