Connect with us

Tsaro

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta kama wani matashi kan zargin garkuwa da wani yaro

Published

on

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta ce ta kama wani matashi Hassan Umar Gwammaja mai shekaru 26, kan zargin garkuwa da wani yaro don neman kuɗin fansa.

Mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan jihar CSP Abdullahi Haruna Kiyawa ne ya bayyana hakan a wani sakon murya da ya wallafa a shafin sa na Facebook.

Ya ce an kama wanda ake zargin ne bayan ya amsa laifin sace yaron a Unguwar Gwammaja, wanda daga bisani aka sako shi bayan biya kudin fansa har Naira miliyan daya.

Matashin da ake zargin mai suna Hassan Umar Gwammaja ya ce matsin tattalin arziki ne yasa shi aikata wannan aiki.

                                        

CSP Abdullahi Haruna Kiyawa ya ce da zarar sun kammala bincike zasu mika wanda ake zargin a gaban kotu.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!