Connect with us

Labarai

Kano: An samu tashin Gobara a gidan Mai na Al-Ihsan da ke Sharada

Published

on

A daran ranar Alhamis din makon nan ne Gobara ta tashin a gidan Mai na Al-Ihsan da ke kan titin Sharada, a Kano.

Gobarar ta tashi ne da misalin ƙarfe 11:00 zuwa 12:00 na dare a daidai lokacin da ake tsaka da  sauke man Fetur.

Shaidun gani da ido sun bayyana cewa, jami’an hukumar kashe gobara sun isa wurin  domin dakile yaduwar wutar, inda kuma ba tare da bata lokaci ba suka samu nasara wajen hana gobarar yin barna mai yawa.

Guda daga cikin wadanda suka shaida faruwar tashin gobarar, Bilyaminu Musa Gwale, ya bayyana wa Freedom Radio musabbabin tashin gobara, inda ya ce, wani mai sayar da Shayi a kusa da gidan man ne ya zubar da Garwashi a daidai lokacin da ake tsaka da sauke man inda bayan ya zuba wutar a cikin kwata sakamakon cewa babu ruwa a kwatar sai kawai wutar ta tashi.

Ya kara da cewa, a nan ne suka yi gaggawar yin amfani da hodar kashe gobara wadda aka tanada a gidan man suka fara kashe wutar.             

Haka kuma Bilyaminu Musa Gwale, ya tabbatar da cewa, babu asarar rai ko jikkata sakamakon gobarar, kana wutar ba ta yi wata babbar barna ba.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!