Connect with us

Labarai

Kano: Gini ya rufto kan mutanen da suka fake wa ruwan sama

Published

on

Wani ginin bene mai hawa 4 da ba a kammala ba a kan titin Abeadi da ke unguwar Sabon Gari a Kano ya rufto tare da danne wasu mutane waɗanda suka fake wa ruwan sama.

 

Wani shaidar gani da ido ya tabbatar wa da manema labarai cewa, lamarin ya faru ne da yammacin Ranar Lahadi.

 

Ya ce, zuwa karfe 9 na dare an zaƙulo mutane 8 waɗanda aka garzaya da su asibiti cikin mawuyacin hali.

 

Hakan kuma, ya kara da cewa, Sai dai masu aikin ceto sun dakata sakamakon dare da rashin samun motar da za ta yi aikin janye ɓaraguzan ginin.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!