Connect with us

Labarai

Kano: Hisbah ta cafke matar da ake zargi da bai wa matasa mafakar aikata Baɗala

Published

on

Hukumar Hisbah ta jihar Kano, ta kama wata mata da ake zargi da tara matasa a gidanta domin aikata badala a yanki Hotoro Walawai da ke Ƙaramar hukumar Taruani.

Wannan dai na zuwa ne bayan korafe-korafen al’ummar yankin kan wadanda ake zargin.

Mutane 11 da hukumar ta kama sun hadar da maza 4 da kuma mata 7.

Mataimakin babban Kwamandan hukumar ta Hisbah Dakta Muhajiddin Aminuddin, ne ya tabbatar da hakan ga manema labarai.

Matar da ake zargi da bayar da mafaka ga masu aikata laifin mai suna Aisha yar asalin jihar Adamawa da kuma wadanda aka kama yayin sumamen da Hisbah ta kai, sun bayyana nadamarsu bayan sun shiga hannu.

Haka kuma mataimakin babban Kwamandan hukumar ta Hisbah Dakta Muhajiddin Aminuddin ya bukaci al’umma da su ci gaa da bai wa hukumarsu hadin kai wajen yaki da aikata laifuka.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!