Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Hisbah ta yi kame a Kano

Published

on

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta sha alwashin ci gaba da yaƙar masu aikata baɗala a lungu da saƙo na jihar Kano.

Babban kwamandan hukumar Hisbah na jihar Kano Sheikh Muhammad Harun Ibn Sina, shi ne ya bayyana hakan a yau Talata, lokacin da hukumar Hisbah ke holen matasan da ta kama a unguwannin Ɗorayi da Ja’en da kuma Janguza, a sakamakon rahoton sirri da mazauna unguwanin suka bai wa hukumar ta Hisbah, na aikata abubuwan da basu dace ba.

A nasa ɓangaren babban daraktan hukumar Hisbah, Dr. Aliyu Musa Aliyu Kibiya ya ja kunnen matasan da su ƙara jin tsoron Allah domin mutuwa ka iya riskar mutum a kowane lokaci.

Daga cikin matasan da Hisbah ta yi holen su akwai samari da ƴan mata masu shekara 14 zuwa sama, waɗanda suka zo Kano da sunan aikatau.

A ƙarshe hukumar Hisbah ta ce zata aika da matasan zuwa gaban kotu domin yanke musu hukunci kan laifukan da ake zargin su da aikatawa.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!