Connect with us

Labarai

Kano: Hisbah ta kama matasa 5 bisa zargin shirya aure ba bisa ka’ida ba

Published

on

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama wasu matasa maza da mata su biyar bisa zargin gudanar da bikin aure ba tare da amincewar iyaye ko bin ka’idojin aure na Musulunci ba.

 

Mataimakin kwamandan hukumar ta Hisbah, Dakta Mujaheedden Aminuddeen, ne ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa jami’ansu sun dauki matakin ne bayan rahotannin da mazauna yankin da aka shirya auren suka bayar. 

 

Haka kuma, Dakta Mujahiddin Aminuddeen ya bayyana cewa wannan aure ya saba wa koyarwar addinin Musulunci da dokokin jihar Kano.

 

Ya kuma bayyana cewa, hukumar za ta ci gaba da daukar mataki kan duk wanda ya yi aure ba bisa doka ba. 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!