Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Kano na iya fuskantar barazanar zaizayar kasa-NEWMAP

Published

on

Shirin kare zaizayar kasa da alkinta albarkatun ruwa na NEWMAP ya ce, kowane bangare na jihar Kano na fuskantar matsalar zaizayar kasa sakamakon yawaitar tone kasar gini barkatakai da kuma toshe magudanan ruwa.

Shugaban kula da shirin a nan jihar Kano, Malam Musa Shuaibu ne ya bayyana hakan jim kadan bayan kammala shirin barka da hantsi na nan Freedom Radio.

Ya ce, akwai wurare da dama na jihar Kano da suke fuskantar wannan matsala ta zaizayar kasa.

Ya kuma ce, babban abinda ke haifar da toshewar magudanan ruwa a wasu wurare baya rasa nasaba da yadda wasu daga cikin al’umma ke zuba shara a cikin magudanan ruwa barkatai.

Shugaban kula da shirin na NEWMAP ya kuma ce za su ci gaba da wayar da kan al’umma game da illar wannan dabi’a da ke janyo barazana ga muhalli a jihar Kano da ma kasa baki daya.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!