Connect with us

Labarai

Kano: Wasu da ake kyautata zaton ƴan bindiga ne sun shiga Garin Gulu

Published

on

Mazauna garin Gulu da ke yankin ƙaramar hukumar Rimin Gado, sun buƙaci hukumomin tsaro da su gaggauta kai musu dauki, sakamakon yadda ’yan bindiga suka fara kai hari a yankin.

Rahotonni sun bayyana cewa, da misalin ƙarfe 8:30 na daren ranar Alhamis wasu ƴan bindiga dauke da makamai  suka shigo cikin garin tare da yin harbe-harbe don razana mazauna yankin.

A wata tattaunawar da Freedom Radio ta yi ta wayar tarho da Malam Abba Rabi’u Gulu, mazaunin garin, ya tabbatar da faruwar lamarin inda ya ce, sun kai harin ne wani kanti inda suka kwaci kuɗi da kayan masarufi.

Haka kuma ya ƙara da cewa, ɓata garin sun ƙwace wa wata matashiya Waya bayan da suka raunata ta.

Malam Abba ya tabbatar da cewa babu wanda ya rasa ransa, kuma babu wanda aka yi garkuwa da shi, sai dai fargaba da tashin hankali da harin ya haifar wa al’umma Garin.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!