Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Kano

Kano: ‘Yan kasuwa sun koka

Published

on

Wani ‘dan kasuwa a nan Kano ya koka bisa rufe iyakokin Najeriya da gwamnatin tarayya ta yi, inda ya ce adadin mutanen da ke samun na kansu a dalilin shigo da kayayyaki ta iyakokin kasar nan sun kai kimanin mutane 100,000.

Shugaban rukunin kantunan Garba Karfe Alhaji Abba Garba, ne ya bayyana hakan ta cikin shirin Barka da Hantsi na nan Freedom Radio, da ya mayar da hankali kan matsalolin da ‘yan kasuwa ke fuskanta sakamakon rufe iyakokin kasar nan, na kan tudu.

Alhaji Abba Garba ya kuma bayyana cewa za su yi dukkan mai yiwuwa wajen ganin sun zauna da masu ruwa da tsaki wajen samun mafita ta yadda wadanda suka rasa sana’o’in su sakamakon rufe iyakokin za su cigaba da ayyukannsu.

A nasa bangaren shugaban kungiyar matasa ‘yan kasuwa na arewacin Najeriya Alhaji Abubakar Kabir, cewa ya yi kasuwanci a yanzu ya lalace sakamakon rufe iyakokin, har ma ya bukaci gwamnati kan ta saurari bukatun ‘yan kasuwar Najeriya, domin ganin an magance matsalar fatara da talauci da ake ciki.

Ya kuma ce yana da kyau gwamnati ta cigaba da kokarin da take yi wajen ganin an samu ci gaba a bangaren bunkasa tattalin arzikin Najeriya.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!