Connect with us

Labarai

Kano: Yan sanda sun kama mutane 6 bisa zargin satar Adaidaita sahu da babura masu kafa 2

Published

on

Rundunar ƴan sandan Jihar Kano ta kama mutane shida bisa zargin satar baburan adai-daita sahu da babura masu kafa biyu, tare da kwato wasu daga cikinsu.

Rundunar ta bayyana hakan ne ta cikin wata sanarwa da mai magana da yawunta SP  Abdullahi Haruna Kiyawa, ya wallafa a shafinsa na Facebook.

SP  Abdullahi Haruna Kiyawa, ya ce, a ranar 14 ga watan nan da muke ciki na Oktoba ne, jami’an yan sanda suka kama wasu mutane biyu wadanda suka yi yunkurin kwace wa wani matashi Adaidaita Sahu a kan titin zuwa filin jirgin sama bayan da suka bai wa matashi lemo wanda ya sanya shi fita daga hayyacinsa bayan ya sha.

Haka kuma a bayyana cewa zuwa yanzu sun gano baburan Adaidaita Sahu guda 3 da kuma babura masu kafa biyu guda 5.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!