Connect with us

Labarai

Kano: Yan sanda sun tabbatar da mutuwar Baba-Beru

Published

on

Rundinar yan sandan Kano ta tattabatar da mutuwar wani matashi Halifa wanda aka fi sani da Baba Beru wanda ake zarginsa da addabar unguwar Gwammaja da kewaye.

Jami’in hulda da jama’a na rundinar SP Abdullahi Haruna Kiyawa ne ya tabbatar da mutuwar tasa a ta cikin wani sakon murya da ya aikowa Freedom radio.

Kiyawa, ya cem a jiya Talata ne suka samu kiran gaggawa inda aka sanar da su cewa, wanda ya rana ran nasa tare da sauran wasu bata gari sun kai farmaki unguwar Gwammaja, inda bayan isar yan sanda ne suka yi artabu da su da ya kai ga faunatar jami’ain ‘yan sanda biyu tare da matashin Halifa, kuma bayan kai shi asibiti ne aka tabbatar da rasuarsa.

Haka kuma, ta cikin sanarwar, SP Kiyawa ya bukaci mutane da su rika kai rahoton duk wasu bata gari da ke addabar yankunansu.

SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya kuma ce rundinar za ta ci gaba da yin aiki tukuru domin tabbatar da ta kakkabe ayyukan fadace fadacan daba a fadin jihar Kano.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!