Connect with us

Labarai

Kano: Yara 2 sun rasu sakamakon nutsewa a Kwalbati

Published

on

Hukumar Kashe Gobara ta Jihar Kano ta tabbatar da mutuwar yara biyu sakamakon nutsewa a wata Kwalbati da ke garin Hayin Yawa Gada da ke yankin ƙaramar hukumar Tudun Wada ta Jihar Kano.

 

Mai magana da yawun hukumar, ACFO Saminu Yusif Abdullahi, ne ya tabbatar da hakan cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Juma’a.

 

Sanarwar ta bayyana cewa, lamarin ya faru ne ranar Alhamis, da misalin ƙarfe biyu na rana, inda yara biyu, Habu Sani da Haruna Isah, masu shekara 15 suka shiga wanka Kwalbatin da ke kusa da gada, inda suka nutse abin da ya janyo suka rasa ransu.

 

Hukumar ta yi kira ga iyaye da al’umma da su tsawatar wa yara kada su kusanci wuraren da ruwa ke taruwa, don kauce wa irin wannan mummunan lamari.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!