Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Karin Mutane 20 sun kamu da zazzabin Lassa a Nigeriya- NCDC

Published

on

Hukumar dakile cututtuka masu yaduwa ta Nijeriya NCDC ta ce, tsakanin 17 da 23 ga watan Afrilun da ya gabata kimanin mutane 20 ne suka kamu da zazzabin Lassa a Nijeriya.

Hakan na cikin rahoton da hukumar ke fitarwa a kowanne mako kan halin da ake ciki game da cutar.

Haka kuma, hukumar ta NCDC ta ce, tun daga farkon shekarar nan da muke ciki zuwa yanzu a kalla mutane 897 ne suka kamu da cutar ta zazzabin Lassa, yayin da mutane 154 suka rasu sanadiyyar cutar a jihohi 26 na Nigeriya.

NCDC ta kuma ce, an gano yadda cutar zazzabin na Lassan ya bazu a jahohin Ondo da Edo da Bauchi da Taraba sai kuma jihar Gombe a cikin mako guda.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!