Connect with us

Ƙetare

Kashim Shettima ya sake mika bukatar bai wa Najeriya kujera ta dindindin a MDD

Published

on

Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima, ya sake mika bukatar a bai wa Najeriya kujera ta dindindin a gaban Kwamitin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya, a wani bangare na babban taron majalisar karo na 80 da ake gudanarwa a birnin New York na Amurka.

 

Shettima, ya ce, Najeriya na da cancanta saboda gudunmawar da ta dade tana bayarwa wajen samar da zaman lafiya a Afirka da duniya, in da ya buga misali da gudunmawar da kasar ta bayar a kasar  Congo a shekarar 1960 da kuma kasashen Liberia da Saliyo da Sudan da kuma kawo ƙarshen wariyar launin fata a Afirka ta Kudu.

 

Lamarin da masana tsaro ke ganin matsalolin tsaro da cin hanci da halin tattalin arzikin Najeriya na iya zama ƙalubale wajen cimma wannan buri.

 

Duk da haka, Najeriya na ganin kujerar za ta ƙara tasirinta tare da kare muradun Afirka a harkokin duniya.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!