Connect with us

Labarai

Katsina: Mutane 2 sun rasu sakamakon zanga-zangar da matasa suka gudanar

Published

on

Aƙalla mutane biyu ne suka mutu bayan wata zanga-zanga da matasa suka gudanar a ƙauyukan Danjanku, Dantashi da Dayi na ƙaramar hukumar Malumfashi, Jihar Katsina.

Zanga-zangar ya biyo bayan harin da ‘yan bindiga suka kai a ranar Litinin, inda suka kashe mutum ɗaya suka kuma tafi da wasu 17 duk da yarjejeniyar zaman lafiya da ke tsakanin gwamnati da yan fashin dajin. 

Rahotanni sun nuna cewa matasan yankin sun fito zanga-zangar ne da safe inda suka toshe hanyar Funtua–Katsina domin nuna bacin ran su kan tsananin hare-hare da kuma gazawar gwamnati wajen kare su.

Sai dai lamarin ya rikide ya zama tashin hankali bayan isowar jami’an tsaro, inda suka bude wuta suka kashe mutane biyu tare da jikkata wasu biyu. 

Mai unguwar Danjanku, Alhaji Tanimu Almakiyayi, ya tabbatar da faruwar harin inda yace suna rayuwa cikin fargaba, yayin da wasu mazauna suka zargi dakarun tsaro da kashe masu zanga-zangar. 

A wani hari daban a Bakori, an kashe ɗan sanda ɗaya, aka jikkata wasu biyu, yayin da jami’an tsaro suka ce sun hallaka wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne su tara.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!