Connect with us

Labarai

Katsina: Sojoji sun ceto mutane 76 daga hannun yan Bindiga

Published

on

Hukumomi a jihar Katsina sun ce sojoji sun yi nasarar ceto mutane 76 da ‘yan bindiga suka yi garkuwa da su yawancin su kananan yara a wani farmaki da suka kai kan ‘yan ta’addan.

 

Kwamishinan tsaron cikin gida na jihar Katsina Nasiru Mua’azu ya ce farmakin ta sama a yanzu wata sabuwar dabara ce ta wargaza maboyar ‘yan bindigar da kuma kawo karshen kashe kashe da garkuwa da mutane don karbar kudun fansa da suka addabi mutanen da basu ji ba basu gani ba.

 

Ana kyauta zaton mutanen da aka ceto suna daga cikin wadanda ‘yan bindigar suka yi awon gaba da su bayan wani hari da suka kai kan wani masallaci a unguwar Mantau a makon da ya gabata inda suka hallaka mutane 50.

 

Ta’asar ‘yan bindiga da ‘yan Boko Haram tsawon shekaru ya addabi yankunan arewacin Najeriya duk da kokarin da shugaban kasar Bola Ahmed Tinubu da kuma wanda ya gabace shi suka yi na shawo kan hare haren.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!