Connect with us

Ƙetare

Kazamin fada ya barke tsakanin sojin Sudan da mayakan RSF

Published

on

Rahotanni sun bayyana cewar an gwabza  ƙazamin fada a yankin kudancin tsakiyar Sudan tsakanin rundunar sojin kasar da kuma kungiyar RSF.

Sojojin sun ce sun ƙwace garin Mabsouta da ke kudancin Kordofan, amma kuma dakarun rundunar da ke Arewacin Kordofan din na fama da harin jiragen sama marassa matuka.

Mazauna babban birnin – El-Obeid, sun ce sun ga hayaki na tashi daga wani sansanin soji da ke birnin.

Duk wani yunƙuri na dakatar da bude wuta ya ci tura inda bangarorin biyu ke kafewa kan wasu sharudda da ba za su yiwu ba.

Jihohin Kordofan din uku sun kasance fagen-daga a yakin basasar Sudan din na wata talatin , inda yanzu kungiyar ta RSF ta kame Darfur.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!