Connect with us

Labarai

Kebbi: Rundunar yan sanda ta tura jami’ai na musamman don aikin nemo daliban GCSS Maga

Published

on

Rundunar yan sandan kasar nan  ta tura jami’ai na musamman don haɗa kai da sojoji da ‘yan sa-kai wajen nemo ɗaliban da aka sace a makarantar sakandiren ‘yan mata ta Government Girls Comprehensive Secondary School, Maga da ke ƙaramar hukumar Danko/Wasagu ta Jihar Kebbi.

Mai magana da yawun rundunar, CSP Nafiu Abubakar Kotarkwashi, ya ce tawagar na bincike a hanyoyin da ’yan bindiga suka bi da dazuzzuka domin ceto ɗaliban tare da kama waɗanda suka kai harin.

A cewar runduna ’yan sandan, a ranar 17 ga watan Nuwamba, 2025, da misalin ƙarfe 4 na asuba, wasu ’yan bindiga ɗauke da makamai suka kutsa makarantar, suna harbe-harbe.

Rundunar ta ce jami’an ta  da ke wajen sun yi artabu da su, amma ’yan bindigar sun tsallaka katangar makarantar tare da sace ɗalibai 25, baya ga kashe wani mutum mai suna Hassan Makuku, tare da jikkata wani Ali Shehu.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!