Connect with us

Labarai

Kebbi: Yan Bindiga sun kashe mataimakin shugaban makaranta a harin da suka kai

Published

on

Yan bindiga sun kai hari a makarantar sakandaren ‘yan mata ta gwamnati GGCSS, Maga, a yankin Danko Wasagu na Jihar Kebbi, inda suka kashe mataimakin shugaban makarantar, Hassan Yakubu Makuku, tare da sace ɗalibai dahar zuwa yanzu ba a tantance adadinsu ba.

Wani mazaunin Maga, Aliyu Yakubu, ya ce ‘yan bindigar sun dirar wa makarantar ne da misalin ƙarfe 5 na safiyar Litinin inda Harin ya jefa mazauna yankin a cikin firgici

A cewar majiyar shugaban makarantar, Makuku, an harbe shi ne yayin da yake ƙoƙarin hana yan bindigar yin awon gaba da dalibansa .

A lokacin da ake tattara wannan rahoto, rundunar ‘yan sanda ba ta ce komai ba game da lamarin, domin jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, CSP Nafiu Abubakar, bai amsa kiran da wakilin Jaridar Daily Trust yayi masa ba

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!