Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Kotu a jihar Kwara ta yi barazanar aikewa da babban sufeton ‘yansanda Ibrahim Idris gidan yari

Published

on

Wata babbar kotun jihar Kwara da ke da zama a garin Ilorin babban birnin jihar karkashin jagorancin mai shari’a Ibrahim Yusuf, ta yi barazanar aikawa da sufeto janar na ‘yansandan kasar nan Ibrahim Idris gidan yari matukar ya ci gaba da raina umarnin kotu.

Kotun dai ta zargi Ibrahim Idris da kin bin umarnin da ta bashi na sakin mai taimakawa gwamnan jihar Kwara na musamman kan harkokin siyasa Olalekan Alabi.

Haka zalika kotun dai ta aikawa sufeto janar na ‘yansandan takardar barazanar ta cikin wani kundi mai dauke da sa hannun magatakardar kotun.

Cikin kundin, kotun ta gargadi Ibrahim Idris da cewa ko dai ya bi umarnin da ta bashi a ranar daya ga watan da muke ciki na Agusta ko kuma ya fuskanci fushinta.

Rundunar ‘yansandan kasar nan dai ta kama Olalekan Alabi a ranar Talatin ga watan Mayu sakamakon zargin sa da hannu cikin fashi da makami da aka yi a wasu bankuna a garin Offa da ke jihar ta Kwara.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!