Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Kotu ta ƙi amince wa da buƙatar Malam Abduljabbar

Published

on

Babbar kotun tarayya da ke Gyaɗi-gyaɗi a Kano bisa jagorancin mai shari’a Lewis Alagua ta ƙi amince wa da buƙatar lauyan Malam Abduljabbar Kabara.

Malam Kabara ya shigar da ƙara gaban kotun yana ƙalubalantar matakin sanya masa takunkumin hana wa’azi bisa zargin yana wuce gona da iri.

Yayin zaman kotun na yau Laraba mai shari’a Alagua ya ce, ba za a hana ƴan sanda da Gwamnatin aikinsu ba, saboda haka za a bar su su ɗauki mataki kan abin da suke ganin zai iya kawo barazana ga jama’a.

Wakilin mu na Kotu Bashir Muhammad Inuwa ya rawaito cewa, yanzu haka an ɗage sauraron shari’ar har zuwa ranar 18 ga watan Fabrairu da muke ciki, domin sauraron ɓangaren waɗanda ake ƙara.

Wanda ake ƙarar sun haɗa da Gwamnatin Kano da Babban Mai Shari’a na Kano da Kwamishinan ƴan sanda da hukumar tsaron farin kaya da jami’an Civil Defence.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!