Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Marigayi Audu Baƙo abin kwaikwayo ne ga gwamnonin yanzu – Dr Aisha Ni’ima

Published

on

Malama a sashin nazarin tarihi a jami’ar Bayero da ke Kano ta ce, marigayi tsohon gwamnan Kano Audu Baƙo ya samarwa jihar Kano ci gaba mai ɗumbin yawa a zamanin mulkinsa.

Dakta Aisha Ni’ima Shehu ce ta bayyana hakan ta cikin shirin Barka da Hantsi na Freedom Radio a ranar Juma’a.

 

Malamar ta ce, ta rubuta littafin tarihin tsohon gwamnan Audu Baƙo ne domin irin cigaban da kuma rawar da ya taka wajen bunƙasa tattalin arzikin jihar Kano.

“Ya kawo ci gaba a ɓangaren ilimi domin shi ne ya assasa kwalejin share fagen shiga jami’a da kuma samar da ɗakin karatu na jihar da kuma rukunin masana’antu na Sharaɗa da challawa.”

Ta ƙara da cewa littafin mai taken Jihar kano a Mulkin Audu Bako na ɗauke da babi takwas waɗanda suka ƙunshi tahirin marigayin da kuma irin gudummawar da ya bayar a jihar kano da ƙasa ma najeriya.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!