Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Kotu ta umarci Ganduje daya mayar da Barista Muhyi kan mukaminsa

Published

on

A jiya ne kotun da’ar ma’aikata ta Najeriya da ke zamanta a Kano ta baiwa gwamnatin Kano umarnin mayar da tsohon shugaban hukumar karbar korafe-korafe da yaki da cin hanci da rashawa Barista Muhuyi Magaji Rimingado kan mukaminsa har zuwa kammala sauraron karar da ke gabanta.

Hakan na cikin hukuncin da mai shari’a Edward Esele ya zartar, inda ya ce a yanzu Muhuyi zai ci gaba da rike mukaminsa bayan sauke shi da gwamnatin Kano ta yi a kwanakin baya.

Da yake karin haske kan yadda zaman ya kasance Barista Yusuf Ali Faragai wanda shi ne lauyan Barista Muhuyi Magaji ya yi bayani kamar haka.

https://freedomradionig.com/wp-content/uploads/2023/02/LABARAN-RANA-MUHUYI-SHARIA-14-02-2023.mp3?_=1

Barista Yusuf Ali Faragai kenan da yayi karin bayani kan yadda hukuncin kotun da’ar ma’aikata ta yi na mayar da Muhuyi Magaji Rimingado kan mukaminsa na shugabancin hukumar Anti-Kwarafshin bayan sauke shi da gwamnatin ta yi.

Haka kuma kotun ta sanya ranar 7 ga watan Maris domin ci gaba da sauraren shari’ar.

Rahoton:Halima Wada Sinkin

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!