Connect with us

Labarai

Kotu ta yanke wa Dagaci da abokinsa hukuncin rataya

Published

on

Wata Babbar Kotu a jihar Gombe, ta yanke wa Dagacin Gundumar Bangunji, Sulei Yerima, da Shedrack Aliyu hukuncin kisa ta hanyar rataya, bayan samun su da laifin aikata kisan kai.

Kotun mai lamba 8 da ke zamanta a Gombe, ƙarƙashin jagorancin Mai shari’a Abdulsalam Mohammad, ta ce an same su da laifi ne bayan an tabbatar da tuhumar da ake yi musu.

A hukuncin da ya yanke, alƙalin kotun ya kuma wanke tare da sallamar wasu mutum uku sakamakon rashin isassun hujjoji a kansu  

Tun da farko, an gurfanar da mutanen a gaban kotu ne, bisa laifukan haɗa baki, tayar da hankali, jikkata mutum, da kisan kai.  

 A ƙarshe, kotun ta yanke wa Dagacin Bangunji, Sulei Yerima, da Shedrack Aliyu Kwan hukuncin kisa ta hanyar rataya.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!