Connect with us

Labarai

Kotun ɗa’ar ma’aikata ta buƙaci ƙungiyar NARD ta janye yajin aiki

Published

on

Kotun ɗa’ar ma’aikata da ke zaman ta a Abuja ta bai wa ƙungiyar likitoci masu neman ƙwarewa NARD umarnin janye yajin aikin da suka tsunduma a ranar 2 ga watan Agustan da muke ciki.

Mai shari’a John Targema ne ya bada umarnin a jiya Litinin lokacin da yake bayani ga masu shigar da ƙara kafin zaman kotun.

A cewar sa, kotu ta yi nazari na tsanaki kan ƙarar da aka gabatar gabanta kan ƙungiyar, wanda hakan ne ya sanya kotun ta bada umarnin janye yajin aikin.

Sai dai tuni ƙungiyar NARD ta ayyana cewa ba za ta janye yajin aikin ba, duk da umarnin na kotu.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!