Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Muna kan bakar mu na ƙin biyan albashi ga masu yajin aiki – Buhari

Published

on

Gwamnatin tarayya ta ce, har yanzu tana kan batun ta na ƙin biyan albashi ga likitocin da ke yajin aiki a fadin kasar nan.

Ministan ƙwadago da samar da aikin yi Cris Ngige ne ya bayyana hakan a zantawar sa da manema labarai na fadar shugaban ƙasa a ƙarshen mako.

Ngige ya ce, a shirye ta ke ta janye ƙarar da ta shigar gaban kotun ɗa’ar ma’aikata kan batun yajin aikin da ƙungiyar likitoci masu neman ƙwarewa ke yi, matuƙar za su dawo bakin aiki.

Gwamnati ba ta biyamu albashin watan Agusta ba – NARD

Tun da fari ƙungiyar NARD ta ƙalubalanci gwamnatin tarayya kan ta janye matakin ta na shigar da ƙara gaban kotun ɗa’ar ma’aikata na tabbatar da dokar babu aiki babu biyan albashi ga ma’aikatan.

Ƙungiyar ta zargi gwamnatin tarayya kan rashin sauraron ƙorafe-ƙorafen su gabanin ɗaukan matakin rashin biyan su albashi.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!