Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Addini

Ku rika tallafawa marasa galihu – Dagacin Sharada ga masu hannu da shuni

Published

on

Dagacin Sharada Alhaji Ilyasau Mu’azu Sharada ya bukaci al’ummar musulmi da su sadaukar da wani bangare na dukiyarsu domin tallafawa mabukata.

Alhaji Ilyasu Mu’azu Sharada ya bayyana hakan ne a yayin taron rabon kayan abinci ga marayu dari hudu da gidauniyar Kano Network mai tallafawa marayu dake Unguwar Salanta ta gudanar a makarantar Firamare ta Salanta.

Sannan kuma ya yi kira ga kamfanonin dake Sharada da ba sa taimakawa jama’a da su dage wajen bayar da na su taimakon.

Da yake jawabi shugaban gidauniyar Malam Adam Umar Abu Salim, ya bayyana cewa sun yi rabon kayan tallafin ne don tallafawa marasa galihu.

Wakilinmu Bilal Nasidi Mu’azu ya ruwaito cewa an raba kayan abinci da suka hadar da shinkafa da taliya masara da gero da sukari da kuma magunguna, inda a gefe guda kuma wata mata ta bayar da gudunmawar kudi naira miliyan daya domin rabawa mata jari.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!