Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

An gano ma’aikatan bogi 668 a jihar Gombe – Kwamishina

Published

on

Gwamnatin Jihar Gombe ta sanar da dakatar da ma’aikata 668 da take zaton na bogi ne sakamakon gaza bayyana a gaban kwamitin tantance ma’aikatan jihar don daukar bayanansu a na’ura wato biometric.

Kwamishin kudi da bunkasa tattalin arzikin jihar Muhammad Gambo Magaji ne ya bayyana hakan yayin zantawa da manema labarai kan fara aikin tantancewar.

Muhammad Gambo Magaji ya ce bisa wannan bincike yanzu haka sun samu nasarar alkinta kudi naira miliyan 38 da dubu dari uku, bayan cire sunayen ma’aikatan da suka gaza bayyana.

Ya kuma kara da cewa aikin tantancewar zai ci gaba har sai sun kammala tantance ma’aikatan Jihar baki-daya.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!