Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Kula da albashin ‘yan sandan al’umma ya rataya a wuyan jihohi – Rundunar ‘yan sanda

Published

on

Rundunar ‘yan sandan kasar nan ta ce nauyin kula da albashi da kuma ‘yan kunji-kunji na ‘yan sandan al’umma da gwamnati ke kokarin kirkirowa a kwanan nan, ya rataya ne a wuyar jihohin kasar nan.

Mukaddashin sufeto janar na ‘yan sandan kasar nan mai kula da harkokin bincike na tsare-tsare, Adeleye Oyebade ne ya bayyana haka ya bayyana haka ta cikin wani shirin gidan talabijin na Channels mai taken: ‘Sunrise Daily’.

Ya ce, har gobe ‘yan sandan kasar nan za ta ci gaba da kasancewa guda daya dunkulalliya, ‘yan sandan al’umma da za a dauka za su rika aiki ne na wucin gadi.

DIG Adeleye Oyebade ya kuma ce ‘yan sandan na al’umma da za a dauka aiki zasu gudanar da aiki ne karkashin sashe na arba’in da tara da hamsin na dokokin rundunar ‘yan sandan kasar nan.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!