Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Ƴan Najeriya dubu 76 ne aka kashe cikin shekaru 10 da suka gabata – Gwamnoni.

Published

on

Ƙungiyar gwamnonin ƙasar nan ta ce tsakanin watan Mayun shekarar dubu biyu da goma sha ɗaya zuwa Fabrairun wannan shekara, sama da ƴan Najeriya dubu saba’in da shida ne suka rasa rayukansu sanadiyar ayyukan ƴan tarzoma a sassa daban-daban na ƙasar nan.

 

Shugaban ƙungiyar gwamnonin na Najeriya Kayode Fayemi na jihar Ekiti shine ya bayyana haka a jiya lokacin da ya ke ƙaddamar da wani shirin tsaro da ƙungiyar ta gabatar a birnin tarayya Abuja.

 

Ya ce, ba ya ga kwararar ƙananan makamai zuwa ƙasar nan ba bisa ƙa’ida ba, wadda sanadiyar hakan ta janyo rikice-rikice na ƙabilanci da ta’addanci, al’amura da dama sun sukurkuce sanadiyar hakan.

 

Gwamnan jihar na Ekiti ya kuma ce matsalar rashin tsaron na ci gaba da kawo tarnaki ga ci gaban ƙasar nan

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!