Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Kungiyar kwadago ta ayyana tafiya yajin aiki a fadin Nijeriya

Published

on

Shugaban kungiyar kwadago ta Najeriya, Joe Ajaero ya umarci ma’aikatan gwamnati a kasa da su fara yajin aiki daga ranar Larabar makon gobe.

Ya kuma ba da umarnin cewa gamayyar kungiyoyin da suka kafa kungiyar kwadago ta Nijeriya su kuma za su kasance cikin shiri domin yin zanga-zanga a dukkan sassan babban bankin Nijeriya CBN.

Umarnin ya biyo bayan wa’adin farko da mambobin kwamitin na NLC suka fitar a makon jiya inda suka soki manufofin gwamnatin tarayya na sauyin kudi.

Ya kara da cewa duk da hukuncin da kotun koli ta bayar na barin tsofaffin naira 500 da naira 1000 su rika yawo da sabbin takardun har zuwa ranar 31 ga watan Disamban shekarar da muke ciki, lamarin ya kara ta’azzara saboda ma’aikata ba sa iya samun kudi don biyan bukatun su.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!