Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Kungiyar kwadago zata cigaba da ganawa da gwamnatin tarayya

Published

on

Kungiyar kwadago zata ci gaba da ganawa da gwamnantin tarayya a yau litinin kan batun mafi karancin albashi bayan ganawar da suka yi a ranar juma’ar da ta gabata, wanda aka tashi taron ba tare da an cimma wata matsaya ba.

Kungiyar kwadagon dai na bukatar fadar shugaban kasa ta mika kudurin dokar mafi karancin albashi gaban majalisun tarayyar kasar nan don mayar da shi doka.

Jim kadan bayan kammala taron da kungiyar ta kudanar da gwamnantin tarayya a ranar juma’ar da ta gabata shugaban kungiyar na kasa Ayuba Wabba ya shaida cewa kungiyar zata kuma zama da gwamnantin tarayya a yau litinin.

Ya kuma kara da cewa zasu yi ganawar ta yau ne da misalin karfe 5 na yamma, inda yace badon shirin tattaunawar ba, kungiyar ta shirya tsunduma yajin aiki a yau.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!