Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kasuwanci

Kungiyoyin kishin yan Nijeriya sun maka CBN a Kotu

Published

on

Kungiyoyin kare hakkin dan Adam da sa ido kan harkokin hada-hadar kudaden al’umma SERAP da takwarar ta, ta bibiyar kudaden kasafi ta  BudgIT da ta  kuma kungiyar 136 concerned Nigerians, sun maka Babban bankin kasa  CBN a Kotu, kan tuhumar sa da  ya ayyana sabon tsarin  tsaron Internet na kudaden al’umma da ke asusun ajiyarsu.

Kungiyoyin dai sun maka CBN a kotu ne saboda wani umarnin bankin na baya-bayan nan wanda ya umarci dukkan bankuna da cibiyoyin hada-hadar kudi da su cire harajin tsaron watau Cybersecurity levy kimanin kashi 0.5 cikin 100 akan duk wata hada-hadar kasuwanci ta yanar gizo.

Umarnin, wanda aka bayar a ranar 6 ga Mayun bana, masu shigar da kara sun yi wa karar ta su da lakabi Umurni ba bisa doka ba.

A cewar Kolawole Oluwadare, mataimakin daraktan SERAP, cirewa  mutane ‘yan kudadensu daga asusun ajiyarsu, ya zarce ikon babban bankin na CBN.

Sai dai kai karar Kotun na zuwa ne bayan da Shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu, ya bada umarnin dakatar da daukar kudin kafin zuwa watan Satumba.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!